22 Nuwamba 2025 - 19:03
Source: ABNA24
Labanon: A Ranar 'Yanci Jini Na Ci Gaba Da Kwarara A Kudancin Lebanon 

Ana ci gaba da bukukuwan yan ci kai a Labanon amma Isra'ila Na Ci Gaba Da Zubar Da Jinin a Kudancin kasar… Shahidai biyu a hare-haren sama da aka kai a garuruwan Zawtar al-Sharqiyah da Frun

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Yau ne ake cika shekaru 82 da samun 'yancin kai na Lebanon, duk da haka mamayar Isra'ila na ci gaba da aikata laifukan ta'addanci a kan fararen hula 'yan Lebanon marasa makamai a Kudancin kasar.

Ta'addancin da Isra'ila ke ci gaba da yi a kullum da kuma karya yarjejeniyar tsagaita wuta na ci gaba da wanzuwa. Wakilin tashar Almanar a Kudancin kasar ya ruwaito cewa wani jirgin sama mara matuki na abokan gaba ya kai hari kan wata mota kirar Rapid a kan hanyar da ke tsakanin Zawtar al-Sharqiyah da Mayfadoun, wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya.

Hakanan Jiya da daddare, jiragen yakin Isra'ila sun kai hari kan wata mota a kan hanyar Frun, wanda hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya, a cewar Ma'aikatar Lafiya ta Lebanon.

Bugu da kari, jiragen yakin abokan gaba sun kai hare-hare biyu a wajen Shamshtar, yammacin Baalbek, a cewar wakilin Al-Manar, wanda ya yi daidai da wani hari da aka kai a yankin Mahmoudiyah a kudancin Lebanon. 

Wakilin Al-Manar ya kuma ruwaito cewa, Isra'ila ta kai hari a tsaunukan yankin Jabbour da ke yammacin kwarin Bekaa da kuma yankin Mahmoudiya.

Your Comment

You are replying to: .
captcha